in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ebola ta yi mummunan tasiri ga tattalin arzikin Laberiya, in ji shugabar kasar
2015-01-27 10:02:47 cri

Shugaba Ellen Johnson Sirleaf ta Laberiya, ta ce, cutar Ebola ta yi mummunan tasiri ga tattalin arzikin kasarta.

Sirleaf ta ce, baya ga tattalin arziki, tasirin cutar ya kuma shafi harkokin kiwon lafiya, da na samar da abinci, kasuwanci da sufuri, da kuma zamantakewar al'umma.

Shugaba Sirleaf ta bayyana hakan ne yayin wata ganawa da ta yi da 'yan majalissar kasar.

Da take tsokaci game da alkaluman kididdigar tattalin arziki, Sirleaf ta ce, bullar wannan cuta ya haifar da karuwar ci gaba daga kaso 5.9 bisa dari zuwa kaso 0.4 bisa dari a fannin na tattalin arziki.

Kaza lika shugabar Laberiyan ta ce, ya zama wajibi a gudanar da sauye-sauye ga tsarin tattalin arzikin kasar, muddin ana fatan cimma muradun da aka sanya gaba, a fannonin samar da manyan ababen more rayuwa.

Ta ce, akwai bukatar kara zuba jari a fannonin dake bunkasa tattalin arziki, a kuma gudanar da sauye-sauye a harkokin gudanarwa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China