in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi shiga-tsakani kan batun Sudan ta Kudu don daukar alhakin kanta kan harkokin kasa da kasa
2015-01-12 16:35:04 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi bayani ga 'yan jarida game da zargin ko Sin ta yi shiga-tsakani kan batun Sudan don samun moriyar man fetur ko a'a inda ya ce, kasar Sin ta yi shiga-tsakani kan matsala a tsakanin Sudan da Sudan ta Kudu don daukar alhakin kanta kan harkokin kasa da kasa, ba don samun moriyarta ba.

Wang Yi wanda ya yi wannan bayanin a kasar Sudan ranar Lahadi ya ce, a shekarun baya, kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen taimakawa warware matsalar Sudan bisa bukatun kasar Sudan, da daidaiton da kasa da kasa suka cimma, da kudurin da kwamitin sulhu na MDD ya zartas.

Minista Wang Yi ya ce, Sin tana yi hadin gwiwa tare da Sudan da Sudan ta Kudu a fannin man fetur, abin da ke samar da moriya ga dukkaninsu. Amma idan yake-yake ko tashin hankalin da aka samu suka yi tasiri ga sha'anin samar da man fetur, da farko za a kawo illa ga jama'ar Sudan da ta Sudan ta Kudu, babu shakka kasar Sin ba ta son gan irin wannan hali. Ya kuma tabbatar da cewa, kasar Sin ta yi shiga-tsakani kan matsala a tsakanin Sudan da Sudan ta Kudu don daukar alhakin kanta kan harkokin kasa da kasa, ba don samun moriyarta ba. Don haka, a matsayinta na abokiyar Sudan da Sudan ta Kudu, Sin za ta ci gaba da yin kokari wajen daukar alhakinta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China