in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da sabon shirin yaki da ayyukan ta'addanci a Najieriya
2015-01-17 16:30:38 cri
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta kaddamar da wani sabon shirin yaki da ayyukan ta da kayar-baya, da dakile yaduwar tsattsauran ra'ayi tsakanin al'ummar kasar.

Shirin wanda aka kaddamar a jiya Jumma'a dai zai maida hankali ne ga wayar da kan jama'a, game da illar dake tattare da ayyukan ta'addanci, da kuma barazanar da tashe-tashen hankula ke haifarwa.

Da yake yiwa manema labaru, da sauran masu ruwa da tsaki karin haske game da shirin, babban mashawarcin shugaban kasar kan harkokin tsaro Sambo Dasuki, ya ce kungiyar tarayyar Turai ta EU, da wasu hukumomin kasa da kasa ne za su dauki nauyin shirin.

Dasuki ya ce karkashin wannan shiri, za a fadada ayyukan wayar da kan jama'a, game da matakan da gwamnati ke dauka a wannan fanni, ciki hadda matakan hana karkatar da kwakwalen jama'a, da baiwa masu tada kayar baya damar fita daga kungiyoyin ta'adda, da kuma sauran matakan yada muhimman bayanai tsakankanin al'umma.

Kazalika mashawarcin na shugaban Najeriya, ya ce za a rika tattara bayanai game da mabiya darikun addinai daban daban, da kididdigar yawan su, da wuraren ibada, tare da tantance irin akidun da ake yadawa mabiya. Ya ce ma'aikatar tsaron kasar za ta shigar da wasu sassanta, da suka jibanci harkokin fararen hula cikin shirin, domin tabbatar da nasararsa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China