Babban jami'i mai kula da hukumar bayar da agajin gaggawa NEMA Abdulsalam Mohammaed ya shaida ma manema labarai a ranar jumma'an nan cewa an riga an kai gawawwakin wadanda suka mutu dakin ajiye su a asibiti.
Abdulsalam Mohammed yace mutane 47 kuma da suka ji rauni suna karban jinya a asibitn kwararru na jami'ar Jos,asibitin kwararru na jami'ar Bingham da kuma asibitin our lady of apostle duka a cikin garin na Jos.(Fatimah Jibril)