in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalissar dokokin Chadi ta amince da tura sojojin kasar zuwa Kamaru da Najeriya
2015-01-17 16:22:31 cri
Majalissar dokokin kasar Chadi, ta amince da kudurin gwamnatin kasan na tura dakarun soji zuwa Kamaru, da tarayyar Najeriya, a wani mataki na karfafa yakin da kasashen ke yi da kungiyar nan ta Boko Haram.

A yayin zaman majalissar dokokin na ranar Juma'a ne dai aka amince da wannan kuduri, wanda ya biyo bayan ganawar da manhukuntan Chadin suka yi, da tawagar kasar Kamaru karkashin jagorancin ministan tsaron kasar Alain Mebe Ngo'o, da kuma wata tawagar gwamnatin Najeriya.

Wata sanarwar da fadar gwamnatin kasar Kamaru ta fitar a ranar Alhamis, ta rawaito shugaba Paul Biya, na jinjinawa 'yan uwantaka da hadin gwiwa da gwamnatocin Kamaru da Chadi ke nunawa juna, musamman a fannin tabbatar da tsaro, da kokarin wanzar da zaman lafiya da lumana a kasashen.

Shugaba Biya ya ce, kamata ya yi sauran kasashen duniya su ba da nasu tallafi ga Kamaru, da ma sauran kasashen dake yankin tafkin Chadi, a kokarin da ake yi na murkushe kungiyar Boko Haram. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China