in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin sa hannu kan takardar mika cibiyar horon matan Chadi da Sin ta kafa
2014-09-12 14:37:00 cri
A yammacin jiya Alhamis 11 ga wata ne aka yi bikin sa hannu kan takardar mika cibiyar horon matan kasar Chadi da Sin ta kafa kyauta a birnin Ndjamena, hedkwatar kasar.

Jakadan Sin a Chadi Hu Zhiqiang ne ya rattaba hannu kan takardar mika cibiyar, shi tare da ministan kiwon lafiya na Chadi Ngariera Rimadjita wanda ya wakilci kasar sa.

Cikin jawabin sa ya yin bikin Mr. Rimadjita ya ce wannan cibiya ta horas da mata, cibiya ce irinta ta farko da aka kafa domin mata tun bayan da aka samu 'yancin kan kasar tsawon sama da shekaru 50, don haka take da muhimmanci kwarai a tarihin kasar. Ya ce a madadin gwamnatin kasar, ya na godiya ga gwamnatin Sin game da kokarin ta na sa kaimi ga bunkasar harkokin mata a Chadi, da fatan za a karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannonin kiwon lafiya, da bunkasar ayyukan zamantakewar al'umma.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China