in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na son yin hadin gwiwa da kasashen da abin ya shafa wajen yaki da 'yan ta'adda
2015-01-15 20:23:34 cri
Yau Alhamis 15 ga wata, a yayin taron manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing, manema labarai sun yi tambaya cewa, an sami labarin cewa, kasar Sin da kasar Turkiya na hadin gwiwa wajen kama wadanda suka aikata laifuffukan ta'addanci a jihar Xinjiang, wannan labarin gaskiya ne ko a'a, sa'an nan kuma ko kasar Sin za ta aike da wasu zuwa kasar Turkiya domin kama wadannan 'yan ta'adda?

Dangane da wannan, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya ce, a halin yanzu, 'yan ta'addan gabashin Turkistan na haifar da kalubalen tsaro a jihar Xinjiang, kuma haka ba kawai babban kalubale ne na tsaro da zaman karko ga kasar Sin ba, kalubalen tsaro ne ga gamayyar kasa da kasa. Aikin yaki da ta'addanci alhaki ne da ya rataya a wuyan gamayyar kasa da kasa, kasar Sin na son yin hadin gwiwa da kasashen da abin ya shafa kan wannan aiki da kuma yaki da 'yan ta'addan gabashin Turkistan. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China