in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da zaben shugaba da na majalisar dokokin kasar Sudan
2014-12-01 15:59:49 cri
Shugaban kasar Sudan Omar Al-Bashir ya sanar da cewa, za a gudanar da babban zaben kasar a ranar 2 ga watan Afrilun shekara mai zuwa, duk kuwa da kiraye- kirayen da wasu ke yi na jinkirta zaben.

Shugaba Al-Bashir wanda ya bayyana hakan yayin wani taron manema labaru, ya jaddada cewa za a gudanar da zaben kamar yadda aka tsara a baya. Ya ce duk wani dan jam'iyyar NCP mai mulkin kasar da ya bayyana burin jinkirta zaben, hakan ra'ayi ne na kashin kai, amma ba na jam'iyyar ta NCP ba.

Wasu jam'iyyun adama na kasar Sudan din dai sun yi kira da a jinkirta zaben shugaban kasa da na 'yan majalisar dokokin kasar, don samun karin lokacin shiri da tattara kudin gudanar da zaben, da kokarin kara samun kuri'u.

Kaza lika wadannan jam'iyyu sun bukaci a wargaza gwamnatin kasar mai ci, a kafa gwamnatin wucin gadi domin gudanar da harkokin kasar kafin zaben. Sai dai shugaba Al-Bashir ya yi watsi da wannan bukatu na jam'iyyun adawa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China