in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi allawadai da harin da aka kaiwa gine ginen man fetur a Libiya
2014-12-28 16:19:05 cri
Tawagar bada tallafi ta MDD a kasar Libiya (MANUL) ta yi allawadai a ranar Asabar da hare-haren da aka sake maimaitawa kan gine-ginen man fetur na kasar Libiya, hare-haren da suka janyo gobara a wuraren ajiyar man fetur dake birnin Sedra.

Tawagar MDD ta yi kashedi kan illolin wannan matsala ga muhalli da kuma tattalin arziki bayan wannan tashin hankali da kuma lalata gine-gine a wannan yankin da ake kira na "ci gaban man fetur", tare da yin kira ga dakarun dake fagen daga da su bada hadin kai domin baiwa 'yan kwana-kwana damar kashe gobarar.

Haka kuma tawagar da a tsagaita bude wuta, har ma da na hare-haren jiragen yaki, dake barazanar bazuwar yakin cikin wannan kasa.

Wadannan hare-haren suna take kudurorin kwamitin sulhu na MDD a kasar Libiya. Man fetur na Libiya na al'ummar kasar Libiya gaba daya kuma shi ne ginshikin tattalin arzikin kasar, in ji MANUL.

Haka kuma tawagar MDD ta yi allawadai da harin ranar Alhamis da wasu mutanen da ba a tantance ba suka kai, da janyo asarar rayuwakan masu gadin tashar wutar lantarki dake kusa da birnin Syrte. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China