in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta fara gwada allurar rigakafin cutar Ebola ta farko a kan mutane
2014-12-29 20:24:52 cri

A yau ne ma'aikatar kiwon lafiya da tsara shirin haihuwa ta kasar Sin ta ba da labari kan shafinta na intanet da cewa, kasar Sin ta fara gwada ingancin allurar rigakafin cutar Ebola ta farko a kan mutane.

An labarta cewa, wannan allura ita ce ta uku a duk fadin duniya, wadda aka fara gwada ta a kan mutane, bayan kasashen Amurka da Canada. Hukumomin da abin ya shafa sun ce, wannan wani babban ci-gaba ne da kasar Sin ta samu wajen yaki da sabbin cututtuka masu yaduwa.(Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China