in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya gana da shugaban kasar Masar
2014-12-24 21:03:52 cri
A yammacin ranar Laraban nan 24 ga wata, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gana da shugaban kasar Masar Abdel-Fattah El-Sisi a babban dakin taron jama'a dake birnin Beijing na Sin.

A lokacin ganawar, firaminista Li ya bayyana cewa, akwai dankon zumunci tsakanin jama'ar kasashen biyu cikin dogon lokaci, wadanda suka yi ta taimakawa juna. A jiya, shugaba Xi Jinping ya yi shawarwari da shugaba El-Sisi tare da samun sakamako mai kyau. Sin na fatan yin kokari tare da Masar, a kokarin bunkasa dangantaka tsakaninsu zuwa wani sabon mataki.

A nasa bangare, shugaba El-Sisi ya yaba bisa ga manufar diplomasiyya da Sin take bi, kuma ya nuna girmamawa ga babban sakamakon da Sin ta samu a fannin bunkasuwa. A don haka Yace kasar Masar na fatan karfafa hadin gwiwa tsakaninta da Sin a duk fannoni, musamman ma a fannonin makamashi, zuba jari da sauransu. Tana kuma maraba da kamfanonin Sin da su shiga manyan ayyuka na kasar, a kokarin samun karin ci gaba a fannin hadin gwiwa da raya dangantaka tsakaninsu.

Bayan haka, a wannan rana kuma, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Zhang Dejiang ya gana da shugaba El-Sisi.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China