in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zambia ta daga a teburin kasashe mafiya iya taka leda a nahiyar Afirka
2014-12-24 10:30:44 cri
Hukumar kwallon kafar duniya FIFA, ta fidda wata sabuwar kididdiga wadda ke nuna cewa a yanzu haka, kasar Zambia na cikin kasashen nahiyar Afirka 10 mafiya kwarewa a fagen taka leda.

Bisa wannan kididdiga, kasar ta Zambia ta daga, daga matsayi na 15 a Afirka, kuma ta 62 a duniya, ya zuwa matsayi na 10 a Afirka ta kuma 46 a duniya.

Kasar ta Zambiya wadda ta lashe kofin nahiyar Afirka na shekarar 2012, ta samu wannan ci gaba ne, sakamakon kwazon da ta nuna a wasannin share fagen gasar nahiyar mai zuwa. Za kuma ta buga wasannin ta ne a rukunin B, tare da kasashen Tunisia, da Cape Verde da janhuriyar Dimokaradiyyar Congo, a gasar da za a fara cikin watan Janairun dake tafe a kasar Equatorial Guinea.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China