in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a fara baiwa malaman addinai tallafi a yankin Ningxia na kasar Sin
2014-12-20 16:19:15 cri
Mahukuntan yankin Ningxia Hui mai cin gashin kansa, sun bayyana cewa daga farkon shekara mai zuwa za a fara baiwa malaman addinan yankin, da suka hada da limaman masallatai, da na majami'u, da na mabiya addinin Budda tallafin kudade.

Rahotanni sun bayyana cewa za a rika baiwa jagororin addinan tallafin kudi a kowane wata tun daga watan Janairun dake tafe, ko da yake sun ce wadanda aka samu da karya dokokin da suka shafi addini za su rasa damarsu ta karbar tallafin, kana mahukuntan yankin ba su bayyana dalilin fito da wannan tsari ba.

Ana dai sa ran gudanar da wannan tsari na gwaji a tsahon shekara guda.

Yankin Ningxia dai na kunshe ne da al'ummar karamar kabilar Hui, kuma kaso daya bisa uku na daukacin al'ummar yankinsu miliyan 6 da rabi musulmi ne, akwai kuma masallatai sama da 3,700 a yankin, baya ga sauran majami'u da kuma wuraren bauta na addinin Budda. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China