in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi MDD ta marawa AU baya wajen bunkasa manufofin kiyaye zaman lafiya
2014-12-17 16:15:21 cri
Zaunannen wakilin Sin dake MDD Liu Jieyi ya ce kamata ya yi MDD ta girmama fatan kasashen Afirka, tare da marawa kungiyar AU baya, a kokarinta na kiyaye zaman lafiya da lumana a nahiyar Afirka.

Mr. Liu ya bayyana hakan ne yayin taron kwamitin sulhun MDD kan hadin gwiwa da kungiyar ta AU a fannin kiyaye zaman lafiya, wanda ya gudana a ranar 16 ga watan nan.

Ya ce kungiyar AU ce ke da bayanai da dabarun yadda za a warware matsaloli a yankunanta, bisa la'akari da matsayin kasashen na Afirka, da shirye-shiryen da ake da su na warware matsalolin nahiyar. Don haka kamata ya yi kwamitin sulhun MDDr ya yi la'akari tare da nuna goyon baya ga kungiyar ta AU, a kokarin shawo kan matsalolin dake haddasa rikice-rikice, da sauraron ra'ayoyi, da shawarwari daga kungiyar ta AU. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China