in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ma'aikatar tsaron kasar Sin ta nemi kasar Amurka da ta daina sayar wa yankin Taiwan makamai
2014-12-19 20:42:41 cri
A jiya 18 ga watan Disamba ne, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya sa hannu kan shirin mika wa shugaban kasar Amurka ikon sayar wa yankin Taiwan jiragen ruwan tsaron kan iyaka na soja 4 masu dauke da makamai masu linzami samfurin Oliver Hazard Perry da majalisun dokokin kasar Amurka suka gabatar. Sakamakon haka, wannan shiri ya zama doka.

Game da hakan, Brigedia janar Geng Yansheng, kakakin ma'aikatar tsaron kasar Sin ya sanar da cewa, bangaren Sin ya yi matukar hassala da wannan shiri, wato bangaren Sin yana nan a kan matsayinsa na kin amincewa da kasar Amurka ta sayar wa yankin Taiwan makamai, da matsayinsa na tsaron iyakokinsa, da kwanciyar hankali da cikakken yankin kasar.

Brigedia janar Geng Yansheng ya nuna cewa, da kakkausar harshe bangaren Sin ya nemi kasar Amurka da ta mutunta ainihin moriyar kasar Sin da muhimman abubuwan da take kulawa. Ya kuma nemi kasar Amurka da ta daina sayar wa yankin Taiwan makamai da yin mu'amala ta fuskar aikin soja tsakanin Amurka da yankin Taiwan na kasar Sin, kuma ta daina lalata dangantakar soja dake tsakanin kasashen biyu na Sin da Amurka da rundunoninsu.

Brigedia janar Geng Yansheng ya kara da cewa, bangaren Sin zai kara mai da hankali kan batun, kuma zai dauki matakin mayar da martani a duk halin da ake ciki. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China