in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Sin ta tsaya tsayin daka kan kin amincewa da shisshigin sauran kasashen duniya kan harkokin cikin gida
2013-10-13 17:10:57 cri
Ranar 12 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin Hua Chunying ta amsa tambayar 'yan jarida dangane da kudurin da majalisar dokokin Turai ta zartas da shi kan yankin Taiwan, inda ta furta cewa, harkar yankin Taiwan, harkar cikin gida ce ta kasar Sin, a sabili da haka, gwamnatin kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan kin amincewa da shisshigin sauran kasashen duniya kan wannan batu.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, a ranar 9 ga wata, majalisar dokokin Turai ta zartas da wani kudurin dake shafar kulla huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kungiyar EU da yankin Taiwan, kuma ta yi kira ga kwamitin kungiyar EU da ya kaddamar da yin shawarwari da yankin Taiwan kan yarjejeniyar ba da tabbaci ga zuba jari da shiga kasuwannin juna, a kokarin zurfafa dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin bangarorin biyu.

Game da lamarin, madam Hua ta bayyana cewa, kasar Sin ba za ta nuna bambancin ra'ayi kan kulla huldar tattalin arziki da cinikayya tsakanin jama'ar yankin Taiwan da na kasashen kungiyar EU ba, amma ta ki amincewa da a raya irin wannan hulda tsakanin hukumominsu. Tana fatan majalisar dokokin Turai za ta tsaya tsayin daka kan bin manufar kasar Sin daya tak a duniya, da yin taka-tsamtsam wajen daidaita batutuwan dake shafar yankin Taiwan, da daina ma'amala da hukumomin yankin Taiwan da kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar cinikayya tsakaninta da hukumomin yankin Taiwan. Da fatan majalisar dokokin Turai za ta yi kokarin kyautata dangantaka tsakaninta da kasar Sin a nan gaba.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China