in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 8 suka mutu a wani hari a Najeriya
2014-08-07 20:48:36 cri
Rahotanni daga Najeriya ya tabbatar da cewa a kalla mutane 8 ne suka rasa rayukan su wadansu da dama kuma suka samu raunin sanadiyar wani hari da 'yan kungiytar nan ta boko haram ta kai da rana tsaka a garin Gwoza na jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar a ranar alhamis.

Maharan dai sun abkawa garin na Gwoza mai nisan kilomita 135 daga Maiduguri babban birnin jihar ta Borno wanda kuma ke kan iyaka da kasar Kamaru su ka rika harbin kan mai uwa da wabi,inji wata majiyar sojin kasar. Jonas Mark wani mazaunin garin da ya sha da kyar ya bada labarain cewa a lokacin harin an cinna ma mujami'u 2 wuta, da ofishin karamar hukumar,shaguna da gidaje har ma da caji ofis din 'yan sanda kafin jami'an tsaro su kawo dauki.

A wani labarin kuma mutane 20 suka rasa rayukan su da suka hada da wassu mayaka 10 a wani hari da ake zargin 'yan kungiyar boko haram ce ta kai a kauyen Zigague dake arewacin kasar Kamaru kamar yadda wani jami'in soji ya sheda ma kamfanin dillancin labarai na Xinhua.

Kanar Didier Badjeck shugaban sashin sadarwa na ma'aikatan tsaron kasar ya ce maharan sai da tun da farko suka yi arangama da dakarun sojin Kamaru.Ya yi bayanin cewa harin da suka kai na huce haushi ne da suka afkama wata motar safa mai dauke da fasinjoji wanda kuma nan take suka kashe mutane 10 cikin har da wani sojan ko ta kwana na kasar.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China