in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin ruwa na Sin da Kamaru sun yi atisayen soja na yaki da 'yan fashin teku
2014-06-03 14:53:41 cri

Rundunar sojojin ruwa rukuni na 16 na kasar Sin, da takwarorinsu na kasar Kamaru, sun gudanar da atisayen soja a karon farko a gabar tekun Guinea, domin yaki da 'yan fashin teku.

Atisayen na ranar 2 ga wata dai shi ne irinsa na farko da sojojin ruwan kasashen biyu suka gudanar, bisa kudurin inganta kwarewarsu a fannin kiyaye tsaro a kan teku, da tinkarar barazanar laifukan da suka shafi teku.

Yayin atisayen sojin, dakarun kasashen biyu sun daidaita aikin ba da umurni, da na jibge sojoji da kuma jigilar jiragen ruwa.

Kammala atisayen sojin da ya gudana cikin nasara, da jiragen ruwa rukuni na 16 na Sin suka gudanar, ya kawo karshen ziyarar kwanaki 4 da suka kai Kamaru, inda daga nan kuma za su zarce zuwa kasar Angola. Kasar Kamaru ta kasance tasha ta 5 a Afirka, da jiragen ruwan rukuni na 16 na kasar Sin suka kai ziyara, kafin hakan sun ziyarci kasashen Tunisiya, da Senegal, da Kodivwa, da kuma Nijeriya. (Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China