in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco za ta fuskanci hukunci mai tsanani daga hukumar CAF
2014-12-05 10:02:05 cri
A sakamakon tsoron ta ga yaduwar cutar Ebola, kasar Morocco ta bayyana rashin amincewa ta dauki bakuncin gasar cin kofin Afirka ta shekara mai zuwa, lamarin da kuma ya janyo ma ta hukunci mai tsanani daga hukumar wasannin kwallon kafar Afirka ta CAF.

Kafin hakan dai hukumar ta CAF ta ki amincewa da bukatar Morocco na dage lokacin gudanar gasar, kafin daga bisani a zabi kasar Equatorial Guinea a matsayin wadda za ta maye gurbin Morocco wajen daukar bakuncin gudanar gasar.

A cewar shugaban hukumar CAF Issa Hayatou, daya daga matakan da aka dauka kan Morocco shi ne, hana ta halartar gasar cin kofin na Afirka har karo biyu a nan gaba, matakin da zai haifarwa Moroccon babbar illa a fannin wasanni, musamman a matsayin ta na daya daga cikin manyan kungiyoyi dake da karfi a fannin kwallon kafar nahiyar ta Afirka. Baya ga dakatarwa, za kuma a ci tarar kasar ta Morocco kudi har dala miliyan 20.

Ya zuwa yanzu dai mutane fiye da dubu biyar ne cutar Ebola ta hallaka a wasu kasashen Afirka, wanda hakan ya sanya Morocco nuna damuwa matuka ga yiwuwar yaduwar wannan cuta a kasar ta kafar wannan gasa. Duk kuwa da cewa kasashe uku da suka fi fama da cutar ta Ebola ba za su halarci gasar a wannan karo ba.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China