in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar kwallon kafar Najeriya ajin mata ta lashe kofin Afirka
2014-10-31 10:13:51 cri

Kungiyar kwallon kafar Najeriya ta mata Super Falcons, ta lashe gasar nahiyar Afirka ta bana bayan da ta doke takwarar ta ta kasar Kamaru da ci 2 da nema.

Gasar dai ta bana wadda aka kammala a ranar Asabar a birnin Windhoek na kasar Namibia, ta kasance ta 9, tun bayan da aka fara gudanar da gasar ajin na mata.

'Yan wasan kungiyar Super Falcons Desire Oparanozie, da Asisat Oshoala ne dai suka jefa kwallaye biyun da suka baiwa Najeriyar nasarar da ta samu a wannan karo.

Najeria ce dai ta fi daukar wannan kofi tun bayan kaddamar da shi a shekarar 1998, domin kuwa sau biyu kacal ta rasa nasarar daukar sa, tun da aka fara buga gasar. Wato dai kulaf din na Super Falcons ya lashe wannan kofi har sau 6, inda kasar Equatorial Guinea ta dauka sau biyu a shekarun 2008 da 2012.

A yanzu haka kuma kungiyar ta Super Falcons ta samu gurbin shiga gasar cin kofin duniya ajin mata da za a buga badi a kasar Canada, inda kuma za ta wakilci Afirka tare da kasashen Kamaru da Cote D'Ivoire.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China