in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya yi kiran da a mayar da hankali kan abubuwan da suka fi shafar jama'a
2014-12-02 20:12:03 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya danganta dukkan nasarori da ci gaban da kasar ta samu a manufofinta na yin gyare-gyare da bude kofa ga hikima da hangen nesan jama'a da yadda suke gudanar da abubuwa.

Shugaba Xi ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a taro karo na 7 na babban kwamitin yin gyare-gyare na kasar da aka gudanar yau Talata a nan birnin Beijing, inda ya tabo batun yadda ake samun fahimtar juna tsakanin masu tsara manufofin yin gyare-gyare da yadda ake aiwatar da shirin a yankunan karkara.

Ya ce, wajibi ne hukumomin su mayar da hankali kan batutuwan da suka fi shafar jama'a da batutuwa masu wuyar sha'ani a rayuwar jama'a ta yadda za a tsara hanyoyin tunkarar wadannan batutuwa daga tushe yayin da ake aiwatar da yin kwaskwarima.

Taron na yau wanda ya kuma tattauna batun yin kwaskwarima kan tsarin mallakar filaye da gidaje da kuma bullo da tsarin gina cibiyoyin al'adu na zamani ya samu halartar manyan shugabannin kasar Sin da suka hada da firayin minista Li Keqiang, Liu Yunshan da kuma Zhang Gaoli. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China