in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi ya bayyana burin kasar Sin na samun bunkasa cikin lumana
2014-11-30 16:49:48 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana burin kasarsa na ci gaba da daukar karin matakan samar da damammaki, wadanda za su fadada nasarorin da ake samu cikin hadin gwiwa da sauran sassa, bisa yanayi na lumana da cimma moriyar juna.

Shugaba Xi wanda ya bayyana hakan cikin jawabin da ya gabatar a taron karawa juna sani game da huldar kasashen waje, wanda aka gudanar a ranekun Juma'a da Asabar.

Xi ya jaddada muhimmancin zaman lafiya, da moriyar juna, tare da cimma burikan kasar Sin na bunkasuwa da na tsaro. Yana mai cewa akwai bukatar cimma daidaito a wadannan fannoni.

Kaza lika shugaban kasar ta Sin ya nuna bukatar ci gaba da habaka nasarorin da ake samu na sabunta kasa, da daukaka matsayin Sin, tare da samar da kyakkyawan yanayi da bunkasar huldodin da za su inganta dangantakar Sin da gamayyar kasa da kasa.

"Za mu ci gaba da bin hanyar wanzar da zaman lafiya irin tamu, tare da dogara da kanmu wajen neman bunkasuwa, a yayin da muke ci gaba da ginin kasarmu. Ba za mu kuma taba watsi da hakkokinmu, ko burikan da muka sanya a gaba ba, haka kuma ba za mu bari a dakile manyan manufofinmu ba", a kalaman Shugaba Xi.

Shugaban na kasar Sin ya kuma ce kasarsa za ta ci gaba da goyon bayan dimokaradiyya cikin harkokin diflomasiyya, tare da martaba daukacin manyan manufofin wanzar da zaman lafiyar nan biyar.

Daga nan sai ya sake nanata aniyar Sin ta martaba ikon kasashen duniya na gudanar da mulkin kai bisa ra'ayin al'ummunsu, da hadin gwiwar samar da ci gaba tare, ba tare da la'akari da girma ko karfin kasashen ba. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China