in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukuni na biyu na rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin karo na 17 ya tashi zuwa Liberiya
2014-11-29 17:05:29 cri
A jiya Jumma'a 28 ga wata, rukuni na biyu na rundunar sojan kiyaye zaman lafiya ta Sin karo na 17 ya tashi zuwa Liberiya, domin gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya na MDD. Rukunin na farko mai kunshe da sojoji 268 ya riga ya tashi a ranar 18 ga wata.

Baki daya, rundunar sojan kiyaye zaman lafiya na Sin a Liberiya karo na 17 tana kunshe da sojoji 558, wadanda za su gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya a Liberiya har tsawon watanni 8.

Sin tana gudanar aikin kiyaye zaman lafiya a Liberiya bisa kuduri mai lamba 1509 da kwamitin sulhu na MDD ya zartas. Ta fara wannan aiki ne a watan Disamba na shekarar 2003. A kullum a kan canza sojoji a watanni takwas takwas, kuma wannan ne karo na 16 da aka canza sojojin Sin dake Liberiya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China