in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan kiyaye zaman lafiyar Sin dake Liberia sun taimaka wa kasar wajen yaki da cutar Ebola
2014-11-27 13:54:52 cri
An gudanar da bikin samar da kayayyakin yaki da cutar Ebola a karkashin reshen wata kungiyar musamman na kiyaye zaman lafiya da MDD ta tura wa Greenville na kasar Liberia a ran 25 ga wata, inda rundunar 'yan sandan kiyayen zaman lafiya ta biyu da kasar Sin ta tura wa kasar Liberia ta samar da kayayyakin ga jihar Sinoe ta kasar.

Kayayyakin da aka samar wa jihar a wannan karo sun hada da abin rufe baki, safar hannu, tufafi, abinci da dai sauransu. Daga cikin wadanda suka halarci bukin samar da kayayyakin akwai, Shugaban reshen kungiyar, mai kula da harkokin daidaitawa na kungiyar musamman mai kula da harkokin gaggawa wajen yaki da cutar Ebola ta MDD dake kasar Liberia, da gwamnan jihar Sinoe, da shugaban ofishin 'yan sanda na jihar da wasu jami'an hukumomin kasa da kasa da na jihar Sinoe.

Tun dai a karshen watan Yuni ne, cutar Ebola ke ci gaba da yaduwa a kasar Liberia, wannan ya sa a kwanan baya, 'yan sandan kiyaye zaman lafiyar kasar Sin dake kasar Liberia sun ba da gudunmawar kudi ga kasar, kuma sun yi amfani da kudaden da suka bayar wajen sayen kayayyakin da suka gabatar a ran 25 ga watan da muke ciki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China