in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya nada sabon mai kula da aikin dakile Ebola a Guinea
2014-11-27 10:24:01 cri

Magatakardan MDD Ban Ki-moon ya nada Abdou Dieng na kasar Senegal a matsayin mai kula da hanyoyin da za'a bi a dakile cutar Ebola a kasar Guinea a karkashin tsarin MDD na daukar matakai na gaggawa domin tunkarar cutar Ebola.

A halin da ake ciki, Dieng zai maye gurbin Marcel Rudasingwa. Mataimakin kakakin MDD Farhan Haq, wanda ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ga manema labarai ya ce, Mr. Dieng zai ci gaba da tafiyar da ayyukan MDD a kasar ta Guinea tare da taimakon gwamnatin kasar da sauran kasashe domin kara kaimin yakin da ake yi da cutar Ebola. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China