in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Akwai hasashen kawo karshen yaduwar Ebola na da tsakiyar shekarar badi, in ji Ban Ki-moon
2014-11-22 17:19:26 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya bayyana cewa, mai iyuwa ne a iya kaiwa ga dakile yaduwar cutar Ebola a kasashen yammacin nahiyar Afirka nan da tsakiyar shekarar 2015 mai zuwa, musamman ma idan gamayyar kasashen duniya suka ci gaba da karfafa kwazon su wajen yaki da cutar.

Mr. Ban wanda ya bayyana hakan bayan ganawarsa da shugaban bankin duniya Kim Jim-Yong, da babbar sakatariyar hukumar kiwon lafiyar ta WHO Margaret Chen da ma wasu manyan jami'ai, ya kara da cewa an samu matukar ci gaba a fannoni da dama, a wasu yankunan da aka gudanar da manufofin yaki da cutar ta Ebola. Sai dai bambacin yanayin yaduwar cutar a yankuna daban daban, da yaduwar cutar a kasar Mali, ya sa ana dada nuna matukar damuwa.

Wannan dalili ne a cewarsa ya sanya shi aikewa da Margaret Chen da wasu masana zuwa Mali, domin tattaunawa kan yadda za a kai ga dakile yaduwar cutar a kasar. Kaza lika babban sakataren MDDr ya bukaci cibiyar kula da harkokin cutar Ebola ta MDD, da ta kafa wani ofis na musamman a kasar Mali.

A nata bangare, Margaret Chen ta bayyana cewa, duk da cewa akwai yiwuwar kawo karshen yaduwar cutar Ebola a wasu yankunan yammacin Afirka, akwai bukatar ci gaba da kandagarkin yaduwar cutar a dukkanin nahiyar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China