in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba kasar Sin ya fara ziyara a kasar Fiji
2014-11-21 20:43:12 cri
A yau ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya isa kasar Fiji a ci gaba da ziyarar da yake a kasashe uku dake kudancin tekun Fasific.

Firaministan Fiji Josaia Voreqe da uwargidansa ne suka tarbi shugaba Xi da mai dakinsa a filin saukar jiragen sama na Nadi.

A jawabinsa shugaba Xi ya ce, yana duba hanyoyin hadin gwiwa da za su tattauna da shugabannin kasar Fiji, wadanda za su bunkasa dangantakar kasashen biyu a nan gaba.

Bugu da kari a lokacin da yake Fiji, shugaba Xi zai gana da shugabannin tsibiran kasashe 8 da suka kulla huldar diflomasiya da Sin don tattauna hanyoyin zurfafa hadin gwiwa da samun moriya tare.

Shugaba Xi ya ce, Sin na daukar tsibiran kasashen a matsayin abokai na kwarai kuma za su yi aiki tare don inganta makomar dangantakarsu a nan gaba.

Ya kuma jaddada kudurin kasar Sin na goyon bayan al'ummar kasashen tsibiran a kokarin da suke yi na samun bunkasuwar da za ta dace da su, kiyaye cikakkun yankuansu da 'yancinsu da kuma muradunsu, sannan su shiga a dama da su a harkokin kasa da kasa da na shiya-shiya kamar sauran kasashe. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China