in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta musunta labarin da kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya suka bayar cewa Sin ba ta yi kokarin yaki da cutar Ebola ba
2014-11-18 15:10:28 cri

Game da labarin da wasu kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya suka bayar cewa kasar Sin ba ta yi cikakken kokari wajen yaki da cutar Ebola ba, kakakin ma'aikatar harkokin ciniki ta kasar Sin Shen Danyang ya bayyana a ranar 18 ga wata cewa, gaskiya dokin karfe.

Shen Danyang ya bayyana hakan a gun taron manema labaru da ma'aikatar harkokin ciniki ta kasar Sin ta gudanar a wannan rana. Tun daga farkon shekarar bana, an samu barkewar cutar Ebola a wasu kasashen yammacin Afirka bi da bi. Daga bisani gwamnatin kasar Sin ta samar musu da tallafi har sau hudu da yawansu ya kai kudin Sin Yuan miliyan 750. Amma wasu kafofin watsa labaru na kasashen yammacin duniya sun bayar da labarin cewa, gudummawar da kasar Sin ta bayar ba ta taka kara ta karya ba.

Game da zancen, Shen Danyang ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin ta samar da gudummawa mafi amfani, kuma ta cika alkawarinta, don haka gwamnatocin kasashen da jama'ar da suka karbi gudummawar har ma da gamayyar kasa da kasa sun nuna yabo ga kasar Sin sosai.

Ban da wannan kuma, Shen Danyang ya yi nuni da cewa, kasar Sin tana daya daga cikin kasashen da suka fi samar da kudin taimako ga kasashe masu fama da cutar Ebola. Ana yin amfani da wadannan kudi a fannonin samar da kayayyakin rigakafi da yaki da cutar, samar da kudi da abinci, tura rukunonin masanan kiwon lafiya da likitoci, taimakawa wajen gina gidan gwaji da cibiyar bada jinya ga masu kamu da cutar a kasashe masu fama da cutar da dai sauransu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China