in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da mutum-mutumin Nelson Mandela a fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu
2013-12-17 14:53:39 cri

An yi bikin kaddamar da mutum-mutumin tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu Nelson Mandela a ranar 16 ga watan nan, a fadar gwamnatin kasar dake birnin Pretoria.

A gun bikin, shugaban kasar Afrika ta Kudu Jacob Zuma, ya bayyana cewa, mutum-mutumin yana alamta Nelson Mandela na rungume da kasar Afrika ta Kudu, da al'ummar ta, wanda ya nuna cewa jama'ar kasar Afrika ta Kudu suna da hadin kai game da bin turbar demokuradiyya.

Shi ma a nasa tsokaci don gane da hakan, ministan kula da harkokin fasahohi da al'adun kasar Mashati Lai cewa ya yi, dalilin da ya sa aka kafa mutum-mutumin Nelson Mandela shi ne, tunawa da kokarin da ya yi a duk rayuwarsa wajen samar da 'yanci, da neman sulhuntawa tsakanin kabilun kasar daban daban.

An ce tsayin mutum-mutumin na Mandela ya kai kimanin mitoci 9, an kuma kafa shi ne a wani dandamalin dake gaban fadar shugaban kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China