in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya gana da takwaransa na Amurka
2014-11-08 16:47:16 cri
Jiya Jumma'a 7 ga wata da dare, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da takwaran aikinsa na kasar Amurka John Forbes Kerry, wanda ya zo nan kasar Sin don halartar taron ministocin kungiyar APEC ta hadin kan tattalin arzikin Asiya da tekun Pasific a nan birnin Beijing.

A yayin ganawarsu a wannan rana, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin na mai da hankali sosai kan ziyarar aikin da shugaban kasar Amurka Barack Obama zai kawo a kasar Sin da kuma sa ran da ake yi zai halarci kwarya-kwaryan taron shugabannin kungiyar APEC. Ana fatan kasashen biyu za su iya dukufa tare don cimma nasarar ziyarar aikin da shugaba Obama zai gudanar a kasar Sin, da kuma ganawar shugabannin biyu, ta yadda za a iya kyautata dangantakar kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi.

A nasa bangaren kuma, John Kerry ya bayyana cewa, goyon bayan da kasar Sin da kuma kasar Amurka suke baiwa juna, musamman kan manyan harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya ya dace matuka da moriyar kasashen biyu. Mr. Obama na sa rai sosai kan ziyarar aikin da zai kai a kasar Sin, kuma kasar Amurka na muradin hadin gwiwa da kasar Sin domin samun kyakkyawan sakamako dangane da ziyarar aikin shugaba Obama a kasar Sin, da kuma bunkasa sabuwar dangantakar manyan kasashen Sin da Amurka . (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China