in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya kalubalanci sojojin kasar Burkina Faso da su mika iko ga fararen hula
2014-11-06 15:02:24 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya bayar da wata sanarwa a ranar 5 ga wata, inda ya kalubalanci bangaren soja na kasar Burkina Faso da ya mika iko ga jama'ar kasar, da daukar matakai wajen maido da tsarin mulkin kasar cikin hanzari.

Sanarwar ta bayyana cewa, kwamitin sulhu ya kalubalanci sojojin tsaron kasar Burkina Faso da su mika iko ga gwamnatin rikon kwarya dake karkashin jagorancin fararen hula, da kuma daukar matakai domin maido da odar tsarin mulkin kasar ba tare da bata lokaci ba. Kwamitin sulhu ya yi kira ga bangarori daban daban dake kasar da su yi kokari wajen samun zaman lafiya da demokuradiyya, da gudanar da zabe bisa tsarin mulkin kasar cikin 'yanci, da adalci, da kawar da bambance-bambance. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China