in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu zanga-zanga a Burkina Faso sun bukaci Kouame Lougue da ya jagoranci gwamnatin rikon kwaryar kasar
2014-11-01 21:05:07 cri
Dubun dubatar masu zanga-zanga a Burkina Faso sun yi Allah wadai, da bayyana sunan babban hafsan sojin kasar janar Honore Nabere Traore, a matsayin wanda zai jagoranci gwamnatin rikon kwaryar kasar, ya zuwa babban zaben da aka tsara gudanarwa nan da kwanaki 90 masu zuwa.

Dubban masu boren dai sun bayyana Kouame Lougue, tsohon janar a rundunar sojin kasar, kuma tsohon ministan tsaro a matsayin wanda ya fi dacewa ya jagoranci rikon kwaryar, bayan murabus din shugaba Blaise Compaore.

Masu boren dai na kallon Nabere Traore a matsayin daya daga wadanda aka dama da su a rusasshiyar gwamnatin shugaba Compaore, don haka kasancewar sa jagoran gwamnatin rikon kwaryar kasar a yanzu, tamkar komawa gidan jiya ne.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China