in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta samar da kayayyakin ba da agaji ga Guinea Bissau don yaki da Ebola
2014-11-02 14:29:49 cri
An gudanar da bikin mika kayayyakin ba da agaji da kasar Sin ta samar don yaki da cutar Ebola a birnin Bissau dake kasar Guinea Bissau a ranar 31 ga watan Oktoba, inda mukaddashin firaministan kasar Guinea Bissau Baciro Dja da jakadan Sin dake kasar Wang Hua suka halarci bikin.

A gun bikin, Dja wanda ya wakilci gwamnatin kasarsa ta Guinea Bissau da nuna godiya ga gwamnatin kasar Sin domin goyon baya da gudummawa da take bayarwa ga kasarsa a cikin dogon lokaci, ya ce, taimakon da kasar Sin ke samarwa ya kara kwarin gwiwwa ga gwamnatin kasar Guinea Bissau wajen tinkarar cutar Ebola, tare da kara karfin rigakafi da kuma shawo kan cutar.

A nasa bangare, Wang Hua ya bayyana cewa, a watan Afrilu na bana, bisa bukatun gwamnatin wucin gadi ta kasar Guinea Bissau, gwamnatin kasar Sin ta samar mata kayayyakin taimako da darajarsu ta kai Yuan miliyan 1 cikin gaggawa don rigakafin cutar Ebola. A wannan karo, kasar Sin ta kara samar da kayayyakin ba da kariya ga lafiyar jiki da sauran kayayyakin ba da agaji da darajarsu ta kai Yuan miliyan 5 ga kasar.

A cewar jakada Wang Hua, ko da yake ba a tarar da cutar Ebola a kasar Guinea Bissau a halin yanzu ba, amma ana fuskantar hali mai tsanani a wannan fanni a kasashen dake makwabtaka da ita. Don haka kasar Sin tana son yin kokari tare da kasar Guinea Bissau wajen kara yin hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa don taka muhimmiyar rawa wajen hana yaduwar cutar Ebola tare da shawo kan cutar a kasashe masu fama da cutar, har ma a dukkan duniya baki daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China