in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na shugaban Sin ya halarci bikin cika shekaru 50 da samun 'yancin kan Zambia
2014-10-25 16:56:58 cri
Bisa gayyatar da aka yi masa, manzon musamman na shugaban kasar Sin, mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Qiangba Puncog ya halarci bikin murnar cika shekaru 50 da samun 'yancin kan kasar Zambia da aka yi tun ranar 22 zuwa ta 25 ga wata a kasar Zambia, inda ya kuma kai ziyarar aiki a kasar tare da wata tawagar wakilan jama'ar kasar Sin. A yayin ziyararsa a kasar Zambia, Qiangba Puncog ya gana da mukaddashin shugaba da wasu manyan jami'an gwamnatin kasar.

Haka kuma, a madadin shugaba, gwamanti da jama'ar kasar Sin, Qiangba Puncog ya taya wa kasar Zambia murnar cika shekaru 50 da samun 'yancin kan kasa, ya ce, shekarar bana ita ce cika shekaru 50 da kafuwar dangantakar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kasar Zambia, kasar Sin tana son ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasar Zambia wajen karfafa hadin gwiwar kasashen biyu daga dukkan fannoni, karfafa mu'amalar dake tsakanin hukumomin majalisun kasashen biyu, ta yadda za a iya ciyar da dangantakar kasashen biyu zuwa wani sabon matsayi.

Kasar Zambia ta nuna godiya ga halartar wakilan kasar Sin a bikin, ta kuma bayyana fatanta wajen yin hadin gwiwa da kasar Sin don ci gaba da samun kyawawan sakamako bisa hadin gwiwar kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China