in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yankin Kurdawa mai cin gashin kansa na kasar Iraki zai tura sojoji zuwa garin Ayn al-Arab na kasar Syria
2014-10-23 16:15:45 cri

Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Iraki suka bayar, an ce, majalisar dokokin yankin Kurdawa mai cin gashin kansa na kasar Iraki ta zartas da wani kuduri a ranar 22 ga wata, inda ta bai wa gwamnatin yankin dama da iznin tura sojoji zuwa garin Ayn al-Arab na kasar Syria, wanda kungiyar IS take kokarin mamaye da kuma fafata yaki a kewayensa.

Gidan telebijin na kasar Iraki ya bayar da labarin cewa, bisa kudurin da majalisar yankin Kurdawa mai cin gashin kansa na kasar ta zartas a wannan rana da yamma, gwamnatin yankin za ta tura dakarunta masu dauke da manyan makamai zuwa garin Ayn al-Arab cikin hanzari don yaki da kungiyar IS.

Bugu da kari, shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan ya bayyana a ranar 22 ga wata cewa, kasarsa za ta taimakawa dakarun yankin Kurdawa wajen shiga Ayn al-Arab don yaki da kungiyar IS. Amma kasar Turkiya ta ki amincewa da kasar Amurka da ta jefa makamai ga dakarun yankin ta jiragen sama. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China