in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 662 sun mutu a sakamakon harin da kungiyar IS ta kai a birnin Ayn al-Arab
2014-10-17 10:42:33 cri
Hukumar kare hakkin dan Adam ta kasar Syria da cibiyarta ke birnin London ta bayyana a ranar 16 ga wata cewa, tun lokacin da kungiyar IS ta fara kai hari kan birnin Ayn al-Arab dake iyaka da Syria da Turkiya, yawan mutanen da suka mutu a sakamakon harin ya kai 662.

Bisa kididdigar da hukumar ta yi, ya nuna cewa mutanen da suka mutu a sakamakon hari sun hada da dakaru masu tsattsauran ra'ayi 374, da mayakan Kurdawa 268 da kuma fararen hula 20.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, wani jami'in mayakan Kurdawa na kasar Syria ya bayyana a ranar 16 ga wata cewa, bisa taimakon hari ta sama da kasar Amurka da sauran kasashen duniya suka bayar, dakarun Kurdawa sun samu nasara a yakin da suke na kare birnin Ayn al-Arab a kwanakin baya. Ya zuwa yanzu, kungiyar IS ta mallaki kasa da kashi 20 na birnin ne kawai. Jami'in ya kara da cewa, mayakan Kurdawa sun fara yunkurin kwato gabashi da kudu maso yammacin birnin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China