in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An cimma wata yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin gwamnatin Najeriya da kungiyar Boko Haram
2014-10-18 16:01:43 cri
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta sanya hannu kan wata yarjejeniyar tsagaita bude wuta tare da kungiyar kishin islama ta Boko Haram, in ji shugaban rundunar sojojin Najriya , mista Alex Badeh a ranar Jumma'a.

Yarjejeniyar ta shafi kuma sako dalibai 'yan mata fiye da 200 da aka sace a cikin watan Afrilun da ya gabata. An cimma wannan yarjejeniya tsakanin babban sakataren musammun na shugaba Goodluck Jonathan, Hassan Tukur da kuma wakilin kungiyar Boko Haram, Danladi Ahmadu, a cewar kakakin cibiyar watsa labarun kasa, Mike Omeri.

Mista Badeh ya tabbatar da cewa ya baiwa rundunar sojojin kasar umurni da su girmama wannnan yarjejeniyar tsagaita bude wuta.

A nata bangare, kungiyar Boko Haram ta ba da tabbacin cewa dukkan dalibai 'yan mata da sauran wasu mutanen da aka sace suna nan cikin koshin lafiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China