in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya yi alkawarin kare rayukan al'ummar kasar
2014-10-02 16:21:26 cri
Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya sake baiwa al'ummar kasar tabbacin kare rayukansu duk da fargabar da ake ta hare-haren da kungiyar nan ta Boko Haram ke kaiwa a sassan kasar,matsalar da ta haifar da babbar barazanar tsaro ga kasar da ke yammacin Afirka.

Shugaban ya bayyana haka ne a jiya Laraba yayin a jawabin da ya yiwa 'yan kasar a bikin cikar kasar shekaru 54 da samun 'yancin kai daga turawan mulkin mallaka inda ya ce, gwamnatinsa ta himmatu wajen kare rayuka da dukiyoyin al'ummarta har ma da 'yan kasashen wajen da ke kasar, sannan ya bukaci kungiyoyin 'yan ta'adda da su hanzarta mika makamansu.

Ya ce, gwamnati ta bullo da wani shiri da nufin sake farfado da tattalin arziki a shiyyar arewa maso gabashin kasar da ke fama da wannan rikici. shirin da shugaban ya ce, ana ci gaba da aiwatar wa a sassa daban-daban na kasar duk da matsalar 'yan ta'addan da ake fuskanta.

Don haka, ya yi kira ga 'yan Najeriya da al'ummomin kasa da kasa da su goyi bayan kokarin da gwamnati da sojojin kasar ke yi na kawo karshen ayyukan ta'addanci a Najeriya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China