in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Somaliya ya yi maraba da yadda kasar Sin ta sake bude ofishin jakadancinta a kasar Somaliya
2014-07-11 16:11:54 cri
A jiya Alhamis 10 ga wata ne mukaddashin jakadan wucin gadi na kasar Sin dake kasar Somaliya Wei Hongtian ya ziyarci shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamaoud, inda ya bayyana cewa, kasar Sin za ta maido da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Somaliya a dukkan fannoni.

Shugaba Mohamaoud ya yi maraba tare da nuna godiya ga kasar Sin da ta sake bude ofishin jakadancinta dake kasar Somaliya, kana ya bayyana cewa, zai ci gaba da samar da yanayin da ya dace ga ofishin jakadancin Sin.

Kasar Somaliya ita ce kasa ta farko da ta kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninta da kasar Sin a yankin gabashin Afirka. Bayan da kasar Somaliya ta fara shiga yakin basasa a shekarar 1991, sai Sin ta janye dukkan jami'ai da ma'aikatan ofishin jakadancinta daga kasar ta Somaliya.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya sanar a ranar 30 ga watan Yuni na bana cewa, Sin ta tsaida kudurin sake bude ofishin jakadancinta dake kasar Somaliya ne da nufin kara inganta dangantakar abokantaka a tsakaninta da Somaliya.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China