in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara samar da hatsi don tallafawa Saliyo
2014-10-10 10:50:02 cri
Daga ranar 8 zuwa 9 ga watan nan da muke ciki, a madadin gwamnatocin kasashen Sin da Saliyo ne jakadan kasar Sin dake kasar Saliyo Zhao Yanbo, da ministan kula da harkokin diplomasiya da hada kai da kasashen ketare na kasar Saliyo Samura Kamara, suka sa hannu kan wata yarjejeniya game da samar da tallafi ga Saliyo da kasar Sin za ta yi.

An ce, tallafin na wannan karo wani sashi ne na ayyukan da kasar Sin ke gudanarwa domin taimakawa kasar Saliyo wajen tinkarar yaduwar cutar Ebola. Hukumar shirin samar da abinci da aikin gona ta MDD (WFP) ce za ta dauki nauyin sayen kayan abincin, da kuma jigilar su zuwa Saliyo, domin taimakawa jama'ar kasar dake fama da cutar Ebola. (Bilkisu)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China