in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta samar da tallafin abinci ga kasashen da ke fama da cutar Ebola
2014-10-09 20:48:55 cri
Ma'aikatar cinikayya ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin ta kulla wata yarjejeniyar samar da tallafin abinci ga kasashen uku da ke fama da cutar Ebola da hukumar samar da abinci da aikin gona ta MDD (WPF).

Wata sanarwa da ma'aikatar ta bayar ta bayyana cewa, kasar Sin za ta samar wa hukumar ta WFP dala miliyan 6 wadanda za a yi amfani da su wajen saye da kuma aika abinci zuwa kasashen Saliyo, Guinea da kuma Liberia.

Wannan wani bangare cikin kashe na uku na tallafin da gwamnatin Sin ke bayarwa don yaki da Ebola kamar yadda shugaba Xi Jinping ya sanar a ranar 18 ga watan Satumba.

A cewar hukumar ta WFP kimanin mutane miliyan 1 ne za su yi fama da matsalar abinci a cikin watanni masu zuwa a wadannan kasashen guda uku sakamakon cutar ta Ebola. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China