in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta samar da karin tallafi ga Guinea wajen kula da cutar Ebola
2014-10-08 16:20:32 cri
Kasashen Sin da Guinea sun sa hannu kan wata yarjejeniya a ranar talata 7 ga wata a Conakry, fadar mulkin kasar Guinea, inda aka tabbatar da niyyar kasar Sin ta samar da karin tallafi ga Guinea don taimaka mata shawo kan cutar Ebola.

A wajen bikin sa hannu, Moustapha Koutoubou SANO, ministan hulda da kasa da kasa na kasar Guinea, ya ce muhimmancin tallafin ya dace da tunawar jama'ar kasar Guinea ta zuriyoyi daban daban.

A nasa bangaren, jakadan kasar Sin dake Guinea, mista Bian Jianqiang, ya ce kasar Sin tana ci gaba da kokarin tallafawa kasashen Afirka a kokarinsu na shawo kan cutar Ebola, inda ta kara samar da tallafin da darajarsa ta kai kudin Sin RMB miliyan 200 ga Guinea, Laberiya, Saliyo, da dai sauransu, tallafin da ya kunshi dalar Amurka miliyan 1 da abinci mai darajar dalar Amurka miliyan 2 da ta ba kasar Guinea. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China