in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya gana da jakadun kasashen waje a kasar 31
2014-09-30 20:36:27 cri
A dab da ranar murnar cika shekaru 65 da kafa Jamhuriyyar jama'ar kasar Sin, firaministan kasar Li Keqiang ya gana da jakadun kasashen waje a Sin guda 31 a nan birnin Beijing a yammacin yau talata 30 ga watan Satumba.

A yayin ganawar da su, Mr. Li ya bayyana cewa, yanzu Sin tana kokarin zurfafa yin kwaskwarima a kasa, da kara bude kofa ga kasashen waje sannan bunkasuwar kasar ta kawo babban zarafi da kasuwanni ga kasashen duniya. Yace don haka Kasar za ta tsaya tsayin daka kan hanyar neman samun bunkasuwa cikin lumana, da ba da gudummawa ga duniya, a kokarin sada zumunci da kasashe makwabta da tabbatar da zaman lafiya a duniya.

A nasu bangare, jakadun sun nuna godiya ga firaminista Li, kuma sun isar da sakonnin taya murnar shugabannin kasashensu ga al'ummar kasar Sin da shugabanninsu. Ban da haka, jakadun sun yaba matuka bisa ga kokarin da Sin take yi na tabbatar da zaman lafiya a duniya, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, da tinkarar kalubale a duniya da sauransu. Daga nan sai suka jaddada cewa, kasashen duniya suna dora muhimmanci sosai kan bunkasa dangantaka tsakaninsu da Sin, da fatan za su karfafa hadin gwiwa tsakaninsu yadda ya kamata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China