in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan takara a zaben shugabancin kasar Afghanistan sun amince a binciki dukkan kuri'un da aka kada
2014-07-14 10:34:18 cri
Sakataren harkokin wajen kasar Amurka John Kerry ya ce 'yan takarar kujerar shugabancin kasar Afghanistan Abdullah Abdullah, da Ashraf Ghani, sun cimma matsaya game da batun tantance dukkanin kuri'un da aka kada yayin babban zaben kasar da ake takaddama a kansa.

Kerry wanda ya bayyana hakan a daren ranar Asabar a birnin Kabul na kasar ta Afghanistan, ya kara da cewa an amince hukumar zaben kasar ta gudanar da bincike kan dukkanin kuri'un ne karkashin sa idon jami'an tawagar MDD.

Rahotanni sun ce bayan ganawarsa da 'yan takarar biyu, Mr. Kerry ya bayyana cewa, bisa shirin da aka yi, sojojin kiyaye zaman lafiya na kasa da kasa dake kasar, da sojojin gwamnati ne za su yi rakiyar akwatunan zaben daga wurare daban daban zuwa birnin Kabul, sa'annan kuma a fara bincike kan kuri'un cikin awoyi 24.

Tun da fari dai hukumar zaben kasar ta Afghanistan, ta gabatar da sakamakon zaben shugaban kasar zagayen biyu ne a ranar 7 ga wata, inda aka bayyana sunan Ghani a matsayin wanda ya samu rinjaye da kaso 56.4 cikin dari na dukkanin kuri'un, yayin da kuma Abdullah ya samu kaso 43.6 cikin dari. Sai dai hukumar ta bayyana cewa an tabka magudi a yayin zagayen zaben na biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China