in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IMF na tunanin samar da kudi ga kasashe uku na yammacin Afirka don sassauta tasirin da cutar Ebola ta yi musu a fannin tattalin arziki
2014-09-25 10:52:13 cri
Jaridar Daily Observer ta kasar Liberia ta bayar da labari a ranar 24 ga watan nan cewa, asusun bada lamuni na duniya wato IMF ya bada shawara ga hukumar darectocin zartaswarsa da a kara samar da kudi dala miliyan 127 ga kasashen Liberia, Guinea da Saliyo, don taimakawa kasashen uku na yammacin Afirka wajen yaki da cutar Ebola,.

Labarin ya bayyana cewa, idan hukumar ta amince da wannan shawara, kudin da za a samar zai taimakawa kasashen uku sosai wajen yaki da cutar Ebola a watanni 6 zuwa 9 masu zuwa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China