in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar farko ta MDD ta isa yammancin Afrika domin yaki da Ebola
2014-09-23 11:57:48 cri

Wata tawagar kwararru ta farko a karkashin shirin MDD na daukar matakin gagggawa a kan cutar Ebola ta isa birnin Accra na kasar Ghana, domin kafa hedkwatarsa a can.

Kakakin MDD, Stephane Dujarric ya bayyana wa manema labarai cewar, Wata tawagar ta dabam ta MDD mai kula da matsalolin da suka shafi kiwon lafiya ita ma ta isa kasar Liberia, wacce ita ce kasa mafi yawan mutane wadanda suka kamu da cutar Ebola.

Kakakin MDD, ya kuma ce, MDD ta kafa wani asusu na hadin gwiwa domin samun gudumuwa daga kasashe a kokarin da ake na tunkarar cutar Ebola. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China