in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kenya na cikin shirin ko ta kwana a kusantowar shekara daya da harin ta'addanci na Westgate
2014-09-21 16:05:02 cri

Kasar Kenya ta sanar a ranar Asabar cewa ta karfafa matakan tsaro a dukkan fadin kasar da kuma kan iyaka da kasar Somaliya a jajibirin cikon shekara daya da harin ta'addancin Westgate, wata cibiyar kasuwanci dake birnin Nairobi, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 67.

Sufeto janar na sandar kasar Kenya, David Kimaiyo, ya bayyana cewa dukkan hedkwatocin 'yan sandar sun samu umurnin karfafa matakan tsaro a cikin manyan biranen kasar.

A ranar 21 ga watan Satumban shekarar 2013, wasu mutane dauke da makamai sun kutsa kai a cikin cibiyar kasuwancin Westgate kana suka afkawa mutanen dake cikin wannan ginin wuta. A cewar mista Kimaiyo, 'yan sandar yankin dake makwabtaka da Somaliya sun karfafa yin sintiri. A Mombasa, birni mafi girma na biyu dake kudu maso gabashin kasar, hukumomin wurin sun tabbatar da cewa birnin na cikin shirin ko ta kwana mafi girma.

"Na ba da umurni ga manyan ofisan 'yan sanda domin tabbatar da tsaro yadda ya kamata a Mombasa da kuma kewayenta", in ji Komandan 'yan sandan Mombasa, Robert Kitur a cikin wata hirarsa da kamfanin dillancin labarai na Xinhua.

Nairobi, Mombasa da wasu sauran birane na kasar Kenya, suna fuskantar hare-haren ta'addanci tun lokacin da kasar ta tura sojojinta a kasar Somliya a karshen shekarar 2011 domin yaki da mayakan kungiyar Al-Chabaab. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China