in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu kada kuri'a sun ki amincewa da 'yancin cin gashin kai na Scotland
2014-09-19 16:11:58 cri
A yau ne aka bayar da sakamakon zaben raba gardama kan neman 'yancin yankin Scotland daga Ingila, kuma sakamakon ya nuna cewa, al'ummar yankin dake adawa da 'yancin cin gashin kan yankin na Scotland a matsayin kasa mai zaman kanta ne suka yi rinjaye.

An kammala jefa kuri'un ne da karfe 10 na daren ranar Alhamis 18 ga wata. Kuma a yau Jumma'a 19 ga wata, aka bayar da sakamakon zaben, inda aka nuna cewa, kashi 55 cikin dari  na masu jefa kuri'un sun ki amincewa da 'yancin yankin na Scotland a matsayin kasa mai cin gashin kanta.

Bisa kididdigar da aka yi, kashi 97 cikin dari na al'ummar yankin da suka cancanci jefa kuri'un ne suka yi rajista, alkalumma na nuni da cewa, wannan shi ne adadin mafi yawa a tarihin zaben da aka taba samu a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China