in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya zartas da kudurin yin kira ga kasa da kasa da su yi yaki da cutar Ebola tare
2014-09-19 11:06:04 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya gudanar da taro cikin gaggawa kan cutar Ebola a ranar 18 ga wata, inda ya ce cutar Ebola ta riga ta kawo barazana ga zaman lafiya da na karko na kasa da kasa, dalilin haka ne aka zartas da wani kudurin yin kira ga kasashe membobin MDD da su samar da gudummawa ga kasashe masu fama da cutar Ebola.

Kudurin ya bayyana cewa, cutar Ebola tana kawo illa ga zaman lafiyar kasashen Liberia, Guinea, Saliyo da Nijeriya, idan har aka kasa dakatar da yaduwarta, watakila ma wannan annoba zata iyar haddasa barkewar rikice-rikicen cikin gida, tsanantar halin tsaro da na siyasa a wadannan kasashen.

A gun taron, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana cewa, za a kafa wata tawagar musamman don samar da guzuri da taimako wajen yaki da cutar Ebola.

Bisa bukatun kayayyaki da MDD take dasu da aka gabatar a wannan mako, an ce ana bukatar gudummawar da ta kai yawan kimanin dala biliyan daya a watanni shida masu zuwa.

Ban da wannan kuma, Ban Ki-moon ya nuna godiya ga kasashen Sin da Cuba da Canada kan rawar a zo a gani da suka taka wajen taimakawa kokarin yaki da cutar Ebola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China