An kashe mutane bakwai na wata tawagar masu fadakar da jama'a ta gwamnati kan cutar Ebola a ranar Alhamis a yankin N'Zerekore, dake tazarar kilomita kusan dubu daga kudancin Conakry, hedkwatar kasar Guinea, in ji ministan sadarwa na kasar Alhousseiny Makanera a ranar Alhamis. Hadarin ya faru ne a ranar Talata da ta gabata a yayin wani bikin wayar da kan jama'a kan yaki da cutar Ebola. An dai gano gawawwakin wadannan mutane bakwai a cikin wani katon rame. (Maman Ada)